SABODA BUDURWA: FITACCEN DAN KWALLON ARSENAL YA TABBATAR DA KARBAR ADDININ MUSLUNCI
Thomas Partey ya bayyana cewa dalilin da ya sa ya
musulunta shi ne, yana matukar son budurwarsa ‘yar kasar
Morocco
Daga: sabitu umar galadima
– Da yake bayar da karin bayani, dan wasan tsakiyar na
Ghana ya tabbatar da cewa babu bambanci tsakanin addinan
biyu
– Thomas yana magana ne yayin wata tattaunawa ta yau da
kullun da 'yar jaridar kafar watsa labarai Nana Aba Anamoah
Ghana - A karshe dai mataimakin kyaftin din kungiyar kwallon
kafa ta maza ta Ghana, Black Stars, Thomas Partey, ya
tabbatar da jita-jitar da ake yadawa na cewa yanzu ya
Musulunta.
A wata ‘yar gajeriyar hira da Nana Aba Anamoah, Thomas ya
bayyana cewa ya yanke shawarar sauya addini ne saboda yana
kaunar budurwarsa kuma babu bambanci tsakanin Kiristanci
da Musulunci.A cewarsa:
"Ina da yarinyar da nake so, na san 'yan matan kodimo na
za su rabu da ni amma ba matsala ... Na girma tare da
Musulmai don haka a karshen dai abu daya ne nakarbwi musulunci
Abin da 'yan Ghana ke cewa
Sorkpor Che Tsatsu yayi sharhi da cewa:
"Zai kare cikin kuka. Ba kirista bane. Ka cika fom ne kawai
don neman addini da Kiristanci. Babu Kirista na gaskiya
da ya sadu da yardar Allah da zai iya canja yakini. Wani
abu ne mu zama Kirista kuma wani abu ne daban mu sadu
da yardar Allah da za ta canja rayuwarka gabaki daya."
Zedkizzy ya ce:
"Kai ne ya kamata ka mai da ita addininka a matsayinka
na mai gida, domin kai kake jagoranta yayin da ta ke bi.
Ina addu'ar kada ta mulke ka."
Comments
Post a Comment